Rahotanni daga Najeriya na cewa an rufe makarantar sakandare ta garin Dapchi dake jihar Yobe a arewa maso gabashin kasar.
Bayanai sun ce an dau wannan matakin ne saboda fargabar hare-haren kungiyar Boko Haram a yankin.
Hukumar makarantar da kungiyar iyayen daliban makarantar ne suka ba da sanarwar rufe makarantar na wani lokaci.
Sai dai ma'aikatar ilimi ta jihar Yobe, ta shaida cewa a hukumance ba a rufe makarantar ba, amma suna da masaniya akan matakin da hukumar makarantar da iyayen daliban suka dauka.
A karshen makon da ya gabata ne wasu da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram, suka kai hari a garin Babban Gida da ke makwabtaka da garin Dapchin.
Idan ana tune a watan Fabrairun 2018 ne wasu 'yan kungiyar Boko Haram suka sace dalibai mata sama da 100 a yankin.
0 Comments